Lin Lin ita ce shugabar kungiyar iyaye mata masu zaman gida ta Nanxiang, wani gari dake yankin Jiading a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin. Kungiyar ita ce irinta ta farko a Shanghai. A lokacin kaddamar da ita a shekarar 2019, kungiyar tana da mambobi 80. Zuwa yanzu kuwa, tana da kusan mambobi 500. Karkashin jagorancin Lin Lin, mambobi mata da dama sun shiga ayyukan raya unguwannin jama’a a shekarun baya-bayan nan. Kana yayin da suke daukar nauye-nauyen taimakawa al’umma, su ma sun samu cikar burikansu.
Farfesa Yakubu Magaji Azare, da Farfesa Aliyu Mu’azu, malamai ne a jami’ar gwamnatin tarayyar Najeriya ta Bayero dake Kano, wadanda suka shigo birnin Beijing na kasar Sin a karshen makon da ya gabata, don halartar taron karawa juna sani na kasa da kasa, kan nazarin harsuna gami da al’adun Afirka na shekara ta 2024...
Don mutunta hakkin dan Adam ana amfani da matakai da dama da kuma yin aiki tare don neman mafita ga matsalolin duniya. Hakan ya sanya aka samar da dokokin hakkin dan Adam na kasa da kasa da sauran dokoki masu nasaba da kare hakkin dan Adam, wadanda suka kasance ginshikan alkawuran kasashe na duniya.
Matan kananan kabilu dake gundumomin Qiandongnan Miao da Dong masu cin gashin kai dake karkashin lardin Guizhou na kudu maso yammacin kasar Sin, sun fara gudanar da wasan kwallon kwando da salo irin na kwallon kafa, inda ake baiwa ‘yan wasa damar yin guje-guje da kwallo, cikin filin wasa ba tare da busa wasu laifuka da aka saba yi cikin wasan a hukumance ba.
A cikin shirinmu na yau za mu duba yadda kasar Sin take kokarin raya masana'antu, da neman samun ci gaban tattalin arziki mai inganci, ta hanyar fasahohi na kare muhallin halittu.