in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na taimaka wa Guinea wajen yaki da cutar Ebola, in ji wani ministan Guinea
2014-08-24 17:05:12 cri
Minista mai lura da harkokin hadin gwiwar kasa da kasa a kasar Guinea Moustapha Koutoubou Sano, ya ce kayayyakin agaji da kasar Sin ta samar ga kasarsa, na matukar taimakawa wajen yaki da cutar Ebola, musamman a daidai wannan lokaci da ake tsaka da daukar karin matakan dakile ci gaba da yaduwar cutar a dukkanin fadin kasar baki daya.

A cewar Mr. Sano a yanzu haka kasar ta Guinea na amfani da kayayyakin agajin kasar ta Sin, wajen gudanar da ayyukan jinya ga wadanda aka tabbatar da cewa suka kamu da cutar, kana kayayyakin sun taimaka wa ma'aikatan jinya wajen hana kamu da cutar.

Bugu da kari a cewar ministan har bayan kaiwa ga karshen yaduwar cutar ta Ebola a wannan karo, za a iya ci gaba da amfani da wadannan kayayyakin agaji.

Daga nan sai Sano ya gabatar da matukar godiyar kasarsa ga mahukuntan kasar Sin bisa wannan taimako, musamman a wannan lokaci da Guinea ke cikin matukar bukatarsa, a kuma gabar da wasu kasashen ba su samar da wani tallafi makamancin wannan ba.

Sano ya kara da cewa wannan taimako na kasar Sin na da muhimmiyar ma'ana ga al'ummomin kasarsa, ya kuma nuna kasancewar kyakkyawar dangantakar sada zumunci mai zurfi tsakanin jama'ar kasashen biyu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Ba a samu fahimtar tsananin tasirin cutar Ebola ba, in ji kungiyar WHO 2014-08-23 16:44:55
v Kungiyar WHO za ta fitar da shirin shawo kan cutar Ebola a makon gobe 2014-08-23 16:04:21
v Senegal ta sake rufe kan iyakarta da kasar Guinea 2014-08-22 16:04:22
v Sin ta haramta bincike kan cutar Ebola ba tare da samun amincewar gwamnati ba 2014-08-22 14:28:26
v WHO na duba yiwuwar samar da magani da alluran rigakafin cutar Ebola 2014-08-22 14:17:37
v Jami'in MDD kan cutar Ebola na ziyarar aiki a yammacin Afrika 2014-08-22 10:02:05
v Bayan yammacin Afirka, babu wani yankin da aka gano cutar Ebola 2014-08-21 14:49:15
v Masanan kimiyya sun fito da maganin yakar kwayar cutar Ebola 2014-08-21 09:49:34
v An yarda a samar da ruwan gwada cutar Ebola da Sin ta fitar 2014-08-20 20:29:08
v Jami'in kula da harkokin cutar Ebola na MDD zai ziyarci yammacin Afirka 2014-08-20 16:02:44
v Akwai alamun dake nuni da cewa, Nigeria da Guinea suna kokari wajen dakilar da yaduwar cutar Ebola 2014-08-20 13:54:16
v Tawagar kwararru masana a kan cutar Ebola daga kasar Sin sun isa Guinea 2014-08-19 10:57:00
v Sin ta nuna goyon baya ga kasar Saliyo wajen yaki da cutar Ebola 2014-08-18 15:29:53
v WHO ta nuna yabo ga taimakon da Sin ta baiwa Afirka wajen yaki da Ebola 2014-08-16 16:24:56
v Masanan kasar Sin sun horar da likitocin kasar Saliyo dake bada jinya ga wadanda suka kamu da cutar Ebola 2014-08-15 15:53:42
v Sin ta gabatar da kayan tallafi ga kasashen Laberiya da Saliyo 2014-08-13 16:20:47
v Masanan kiwon lafiya na kasar Sin sun isa kasar Saliyo 2014-08-13 14:14:10
v Kayayyakin tallafin da Sin ta samar sun isa kasashen Afrika uku dake fama da Ebola 2014-08-13 11:05:04
v Kayayyakin likitanci da Sin ta bada taimako sun isa Guinea 2014-08-12 15:29:12
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China