in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Senegal ta sake rufe kan iyakarta da kasar Guinea
2014-08-22 16:04:22 cri
Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Senegal ta fitar da wata sanarwa a daren ranar 21 ga wata, inda ta bayyana sake rufe kan iyakar kasar da Guinea da zummar hana yaduwar cutar Ebola.

Sanarwar ta ce, bisa la'akari da yadda cutar Ebola ta zama babbar matsalar dake adabar duniya, kasar Senegal ta tsaida kudurin sake rufe kan iyakar kasarta da kasar Guinea. Ban da wannan kuma, ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Senegal ta tsaida hana shigowar jiragen sama da jiragen ruwa daga kasashen Guinea, Saliyo da Liberia zuwa kasar Senegal.

A watan Maris din shekarar bana ne dai, kasar Senegal ta sanar da rufe iyakar kasa a tsakaninta da kasar Guinea dake fama da cutar Ebola, amma kuma aka bude iyakar a watan Mayu. Ya zuwa yanzu, babu wani mutumin kasar Senegal da ya kamu da cutar Ebola.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China