in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta nuna yabo ga taimakon da Sin ta baiwa Afirka wajen yaki da Ebola
2014-08-16 16:24:56 cri
Wani jami'in hukumar kiwon lafiya ta kasa da kasa ta WHO ya bayyana cewa, taimakon gaggawa da gwamnatin kasar Sin ta baiwa yammacin kasashen Afirka na da muhimmiyar ma'ana wajen hana yaduwa da yin rigakafin cutar Ebola a yankin, haka kuma, fasahohin kasar Sin wajen fuskantar da cutar Sars da dai sauran harkokin kiwon lafiya ta gaggawa sun kuma ba da babban taimako wajen hana yaduwar cutar Ebola a Afirka.

Kakakin hukumar Gregory Hartl ya yi matukar godiya ga kasar Sin don karin taimakon kayayyakin agaji da masanan kiwon lafiya da ta tura wa kasashen Afirka a wannan lokaci. Ya ce, fasahohin kasar Sin kan yadda za a iya ba da taimako ga al'ummomin yankin, da kuma hana yaduwar cutar yadda ya kamata suna da muhimmiyar ma'ana ga kasashen da cutar ta shafa a halin yanzu.

Bugu da kari, mataimakin babban sakataren WHO Keiji Fukuda ya nuna cewa, gwamnatin kasar Sin ta mai da hankali sosai kan harkokin kiwon lafiya, lamarin da ya sa ta samu kyakyyawan sakamako kan harkokin binciken cututtuka, samar da labaran da abin ya shafa yadda ya kamata da dai sauransu. Don gane haka, yammacin kasashen nahiyar Afirka suke iya yin koyi daga kasar Sin, kara zuba jari kan ayyukan kiwon lafiya, wanda zai ba da muhimmin taimako ga kasashen wajen yaki da cutar Ebola wadda a halin yanzu, ta riga ta kasance hadarin kiwon lafiya na gaggawa dake janyo hankulan kasa da kasa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China