in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bayan yammacin Afirka, babu wani yankin da aka gano cutar Ebola
2014-08-21 14:49:15 cri
Rahotannin da wasu kasashen suka fitar kwanan baya, sun bayyana cewa, an gano wasu mutanen da suka kamu da cutar Ebola a wasu kasashen duniya, sai dai a jiya Laraba 20 ga wata, hukumar kiwon lafiyar kasa da kasa ta WHO ta sake jaddada cewa, ya zuwa yanzu, ban da kasashen Guinea, Liberia, Saliyo da kuma Nijeriya dake yammacin Afrika, ba a gano wanda ya kamu da cutar Ebola a sauran kasashen duniya ba.

Bisa sabon rahoton da hukumar ta fitar, an ce, ta samu wasu rahotanni cewa, an gano wasu da ake zaton sun kamu da cutar Ebola a wasu kasashe daban, a halin yanzu, tana kokarta wajen gudanar da bincike kan lamarin.

Hukumar WHO ta kuma kara da cewa, cutar ba ta yaduwa ta hanyar iska, dalilin da ya sa, akwai wuya ma'aikatan dake aiki a kamfanonin sufuri musammun ma na jiragen sama su fuskanci barazanar kamuwa da cutar sosai. Hukumar ta yi kira ga wandannan kamfanoni da su tsai da kudurori bisa binciken kimiyya, tare da fatan kuma za su ci gaba da kai kayayyakin agaji da na yau da kullum da jama'ar ke bukata zuwa yammacin kasashen Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China