in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta gabatar da kayan tallafi ga kasashen Laberiya da Saliyo
2014-08-13 16:20:47 cri

Kasar Sin ta mika kayayyakin tallafi ga kasashen Laberiya da Saliyo, domin tinkarar cutar nan mai hadarin gaske ta Ebola.

Yayin bikin mika kayan ga mahukuntan Laberiya da ya gudana a ranar 12 ga watan nan, wanda aka yi a wani ofishin hukumar kula sufurin ruwa, shugaban kasar Laberiya Ellen Johnson Sirleaf, ta bayyana cewa Sin sahihiyar abokiya ce ga kasar ta, wadda ke baiwa kasar taimako a fannonin tattalin arziki, da ilmi, da sha'anin noma, da aikin jiyya, da fannin shari'a da sauransu. Haka kuma a cewar ta Sin na baiwa Laberiya tallafi ciki gaggawa, a duk lokacin da bukatar hakan ta bijiro.

A daya hannun kuma, an gudanar da bikin mika kayayyakin tallafi ga kasar Saliyo, a fadar gwamnatin kasar, inda jakadan Sin dake kasar Zhao Yanbo, da mataimakin ministan kiwon lafiya na kasar suka sanya hannu kan takardar karbar kayayyaki.

A nasa bangare, shugaban kasar Saliyo Ernest Bai Koroma ya ce Sin ta shiga gaban sauran kasashen duniya, wajen baiwa kasar sa tallafin tinkarar cutar Ebola. Don haka ya godewa gwamnatin kasar Sin da jama'arta bisa hakan.

Mr. Koroma ya kara da cewa, Saliyo tana kokarin tinkarar kalubalolin da Ebola ta haifar, za kuma ta yi iyakacin kokarin magance yaduwar wannan cuta cikin makonni masu zuwa, ta hanyar kara zakulo masu dauke da ita, da kafa karin cibiyoyin jiyya, da dai sauran matakai daban daban, ta yadda za a kawar da illar gurgunta tattalin arziki da al'ummar Saliyo ke fuskanta sakamakon yaduwar cutar ta Ebola. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v An dage komawa manyan makarantu a Ghana saboda Ebola 2014-08-13 15:48:11
v WHO ta amince da yin amfani da gwajin magani wajen yin jinya ga mutanen da suka kamu da cutar Ebola 2014-08-13 14:40:57
v MDD ta nada Nabarro a matsayin mai lura da batutuwan da suka shafi cutar Ebola na majalissar 2014-08-13 14:32:19
v Masanan kiwon lafiya na kasar Sin sun isa kasar Saliyo 2014-08-13 14:14:10
v Guinea-Bissau ta rufe kan iyakarta da kasar Guinea sakamakon fargabar yaduwar cutar Ebola 2014-08-13 11:26:10
v Kayayyakin tallafin da Sin ta samar sun isa kasashen Afrika uku dake fama da Ebola 2014-08-13 11:05:04
v Kwararrun kasar Sin sun isa Conakry 2014-08-12 15:30:26
v Gwamnatin Kamaru ta karyata bullowar Ebola a kasarta 2014-08-12 15:29:54
v Kayayyakin likitanci da Sin ta bada taimako sun isa Guinea 2014-08-12 15:29:12
v An dakatar da fasinjojin kasashe uku shiga kasar Gambia 2014-08-12 10:14:20
v Shugaban Najeriya ya alkawarta dakile cutar Ebola 2014-08-12 10:05:10
v An sake samun wanda ya kamu da Ebola a Jihar Lagos 2014-08-11 20:42:56
v An killace mutumin da ake zaton ya kamu da cutar Ebola a kasar Rwanda 2014-08-11 11:09:49
v Kasashen Afirka na kara kokarin hana yaduwar cutar Ebola 2014-08-11 11:06:38
v Dan Najeriyar da aka yiwa gwajin Ebola a Hong Kong ba ya dauke da cutar 2014-08-11 10:56:19
v Masanan kiwon lafiya na Sin na kan hanyar zuwa kasashe uku dake yammacin Afirka 2014-08-10 20:38:03
v Gwamnatin Guinea ta sanar da rufe iyakokinta da Liberia da Saliyo 2014-08-10 16:42:48
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China