in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in kula da harkokin cutar Ebola na MDD zai ziyarci yammacin Afirka
2014-08-20 16:02:44 cri
Babban jami'i mai kula da harkokin da suka shafi cutar Ebola na MDD David Nabarro, ya ce zai ziyarci kasashen yammacin Afirka mafiya fama da cutar Ebola a ran 20 ga watan nan, don ba da taimako ga hukumomin kiwon lafiyar kasashen.

Nabarro wanda ya bayyana hakan a jiya Talata, ya ce kamata ya yi a fidda managartan shirye-shirye a fannonin daban daban, domin fuskantar kalubalen yaduwar wannan cuta.

Ya ce matsalar da ake fama da ita ba ta tsaya ga hukumomin kiwo lafiya kadai ba, domin kuwa ta ba da nasaba da batun zamantakewar al'umma, da tattalin arziki, da kuma harkokin siyasa. Batutuwan da muddin ba a warware su ba, mai iyuwa ne za a fuskanci babban kalubale ga ayyukan jin kai, da na siyasa da tsaro. Don haka ne Mr. Nabarro ya bayyana bukatar nuna goyon baya kan dukkanin harkokin da suka shafi wannan cuta daga dukkanin fannoni.

Babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya nada Mr. Nabarro a matsayin babban jami'i mai kula da harkokin cutar Ebola na MDD ne a ran 12 ga watan da muke ciki. Da ma kuma Mr. Nabarro babban masani ne a fannin harkokin kiwon lafiya, na hukumar lafiya ta duniya WHO. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China