in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta haramta bincike kan cutar Ebola ba tare da samun amincewar gwamnati ba
2014-08-22 14:28:26 cri

Jami'an hukumar lafiya ta kasar Sin sun jaddada a Juma'a cewar, a hana a gudanar da gwaje-gwajen kwayar cutar Ebola a cikin fadin kasar, har sai wadanda suke muradin gudanar da irin wannan gwajin sun samu izinin gwamnati.

Hukumar kula da lafiya da tsarin iyali ta kasar Sin, ta ce, gudanar da gwaji a kan kwayoyin cutar virus da gudanar da aune-aunen cutukan dabbobi, dole ne a gudanar da su a ofishin bincike wanda aka sanyawa magungunan kariya na kwayoyin cutuka.

Hukumar lafiyar ta kasar Sin ta dauki wannan mataki ne domin kara tsaurara matakai sakamakon bullar cutar Ebola, wacce ta kashe mutane fiye da dubu daya a Afrika ta yamma.

Hakazalika hukumar ta ba da umurni cewa, dole ne a tsabtace sharar da aka yi gwajin cutar Ebola, kamin a bisne sharar ta hanyar sa mata magani, kuma hukumar ta bukaci da a yi amfani da sharuddan kariya da suka dace a yayin da ake jigila ko gudanar da gwaje-gwaje a kan cutar Ebola mai saurin kisa. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China