in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Birtaniya sun ba da haddadiyar sanarwa
2014-06-18 16:34:41 cri

Gwamnatin kasar Sin da Birtaniya sun fidda wata haddadiyar sanarwa, wadda ta shafi dangantakar dake tsakanin Sin da Birtaniya a fannoni masu yawa.

Wannan sanarwar da aka fitar a birnin London mai kunshe da sassa 30, ta bayyana karfin da dangantakar sada zumunci tsakanin kasashen ke da ita, musamman a fannin manyan tsare-tsaren hadin gwiwa da ya kasance wani muhimmin kashi cikin manufofin diplomasiyyar kasashen biyu.

Sanarwar ta ce a matsayin kasashen na abokan juna, sun sanya zarafi mai kyau na samun bunkasuwa tare. Baya ga kudurinsu na amincewa da bunkasa mu'ammala tsakanin manyan shugabanninsu, da ingiza hadin kai a fannoni daban-daban, da ma batun ba da jagoranci ga karfafa dangantakar dake tsakaninsu.

Kazalika kasashen biyu, suna darajanta ci gaban da aka samu cikin wasu tsare-tsaren tuntubar juna tsakanin manyan jami'ai, ciki hadda ganawa tsakanin firaministocinsu a wannan shekara, da tattaunawa a fannin tattalin arziki da ciniki, da tsarin yin musanyar ra'ayi kan al'adu, da bayyana ra'ayi bisa manyan tsare-tsare da dai sauransu, matakin da ake fatan zai taimaka wajen bude karin hanyoyin habaka wadannan tsare-tsare.

Bugu da kari kasashen biyu sun amince da shirya tattaunawa a karo na 6, a fannin tattalin arziki da hada-hadar kudi tsakaninsu, a watan Satumbar dake tafe a kasar Birtaniya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga wasu
v Wakilin Sin ya yi kira da a kara yin hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa a fannin aikin gona 2014-06-18 14:17:52
v FAO ta yabawa kasar Sin game da rage yawan masu fama da yunwa kafin cikar wa'adi 2014-06-17 14:22:14
v Tawagar sojin ruwan Sin za ta kai ziyara a Afirka ta Kudu 2014-06-16 10:40:35
v Kasar Sin na fatan karfafa dangantaka da jamhuriyar Congo 2014-06-14 16:32:18
v Firaministan Sin ya gana da shugaban Congo-Brazzaville 2014-06-13 20:42:54
v Shugaban Sin ya bukaci sa kaimi ga yin kwaskwarima kan samar da kuma yin amfani da makamashi 2014-06-13 20:27:40
v Sakataren ofishin kula da kwamitin tsakiya na JKS ya gana da bakin Equatorial Guinea 2014-06-13 10:55:45
v Shugaban kasar Sin ya yi shawarwari da takwaransa na Congo Brazzaville 2014-06-12 20:34:30
v Sin da Birtaniya za su kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa da dama 2014-06-12 14:46:17
v Sin ta bayyana matsayinta kan rahoton da Amurka ta fitar game da harkokin sojan kasar Sin 2014-06-11 20:41:05
v Sin ta yi kira da a kiyaye wani tsarin sararin teku mai jituwa 2014-06-11 20:29:49
v Sin za ta kara hadin gwiwa da sauran kasashe masu tasowa wajen tinkarar sauyin yanayi 2014-06-11 16:02:48
v Sojan ruwa na Sin da na Namibia sun yi atisayen soja kan teku a karon farko 2014-06-11 16:02:01
v Za a kara fahimtar manufar kasa daya, tsarin mulki biyu ta hanyar gabatar da takardar bayani 2014-06-11 15:15:09
v Sin da Rasha sun gabatar da sabon daftarin ka'idoji da ya shafi sararin samaniya 2014-06-11 15:06:58
v Sin ta yi kira da a aiwatar da dokar wanzar da zaman lafiya a kan teku 2014-06-10 15:40:42
v Sin ta mika takarda ga MDD game da matsayinta kan sabanin ta da Vietnam 2014-06-10 10:40:20
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China