Wannan ne dai zango na karshe da tawagar sojojin ruwan ta Sin za ta kai ziyara a nahiyar Afirka, kana shi ne karo na biyu da sojojin ruwan Sin suka kai ziyara a Afirka ta Kudu.
Jakadan Sin dake kasar Afirka ta Kudu Tian Xuejun ya bayyana cewa, a yayin ziyarar, tawagar za ta yi mu'amala tare da sojojin ruwan kasar Afirka ta Kudu, kana jama'ar kasar za su kalli wannan ganawa. Mr. Tian ya yi imani cewa wannan ziyara, za ta kara bunkasa fahimtar juna, da sada zumunci a tsakanin kasashen biyu, tare kuma da sa kaimi ga bunkasuwar dangantakar hadin gwiwa dake tsakanin sojojin kasashen biyu. (Zainab)