in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi kira da a aiwatar da dokar wanzar da zaman lafiya a kan teku
2014-06-10 15:40:42 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wang Min, ya bayyanawa taron cibiyar MDD dake birnin New York cewa, kasar Sin na bukatar a aiwatar da dokar zaman lafiya a kan teku, tare da fatan hawa teburin shawara kai tsaye da kasashen da batun ya shafa, domin kaiwa ga warware matsalar da ake fuskanta a yanzu haka.

An dai gudanar da taron karo na 24 na kasashen da suka amince da yarjejeniyar dokar zaman lafiya a teku ta MDD, a cibiyar MDD a ranar Litinin, domin murnar cika shekaru 20 da daddale wannan yarjejeniya.

Yayin taron shugaban tawagar Sin Wang Min, ya bayyana cewa, yarjejeniyar ta tabbatar da tsarin doka da oda a kan teku, wadda ta samu amincewa daga kasa da kasa. Ya ce cikin shekaru 20 da suka gabata, yarjejeniyar da hukumar kula da harkokin karkashin teku, da kuma kotun kula da dokar teku ta duniya suke aikin zartaswa ta samu nasarori da dama.

Bugu da kari Mr. Wang Min ya jaddada cewa, kasar Sin kasa ce da ke bin dokokin tekun kasa da kasa, tana kuma fatan warware kataddamar da ta shafi hakan cikin lumana. Gwamnatin kasar Sin ta tsaya tsayin daka kan manufar diplomasiyya mai kunshe da zaman lafiya, da bin ka'idojin kundin tsarin MDD, da na yarjejeniyar dokar teku, da warware rikicin teku cikin lumana, da kuma girmama hakkin kasa da kasa na zabin hanyar zaman lafiya don warware rikici. Hanya mafi kyau wajen warware rikici a kan teku dai ita ce, kasashen da rikicin ya shafa su gudanar da shawarwari, bisa tushen girmama tarihi, da dokokin kasa da kasa, kuma wannan ita ce nasarar da yawancin kasashe suka samu a wannan fanni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China