in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a kara yin hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa a fannin aikin gona
2014-06-18 14:17:52 cri
Hukumar abinci da aikin gona FAO ta gudanar da wani taron tattaunawa, game da hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa a ranar 17 ga wata, inda wakilin Sin dake halartar taron ya yi kira da a kara yin hadin gwiwa, a tsakanin kasashen duniya a fannin aikin gona.

Taron na wannan karo dai ya maida hankali ga tattauna nasarorin da FAO, da ma sauran kasashen duniya suka samu yayin da ake aiwatar da hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa a fannin aikin gona. Har ila yau an nazarci hanyoyin da ya dace a bi a wannan fanni a nan gaba. Cikin jawabin da ya gabatar yayin taron, mataimakin ministan harkokin aikin gona na kasar Sin Chen Xiaohua ya ce, rashin tsaro a fannin abinci na haddasa rashin daidaito yayin da ake kokarin samun bunkasuwa a duniya, yana kuma kawo illa ga samun bunkasuwar tattalin arziki, da zaman lafiya a duniya. Don haka, ya zama tilas al'ummomin duniya su yi hadin gwiwa da juna don tinkarar wannan kalubale.

Haka nan Mr. Chen Xiaohua ya ce, kamata ya yi kasashen duniya su dauki nauyin dake wuyansu mabambanta, su kuma taimakawa kasashe masu tasowa wajen bunkasa aikin gona da tabbatar da tsaron abinci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China