in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kara hadin gwiwa da sauran kasashe masu tasowa wajen tinkarar sauyin yanayi
2014-06-11 16:02:48 cri
Mataimakin darektan kwamitin raya kasa da yin kwaskwarima na kasar Sin, Xie Zhenhua ya bayyana a birnin Shenzhen cewa, kasar Sin tana son kara yin hadin gwiwa tare da bangarori daban daban, da aiwatar da ayyukan da aka tsara a takardar tunatarwar hadin gwiwa, tare da kara karfafa hadin gwiwa a tsakanin kudu da kudu, don ba da gudummawa ga duniya wajen tinkarar sauyin yanayi.

A cewar mista Xie Zhenhua, tun daga shekarar 2011, gwamnatin kasar Sin ta kara mai da hankali kan hadin gwiwa tsakaninta da sauran kasashe masu tasowa domin tinkarar sauyin yanayi, kuma ta kebe kudi dalar Amurka miliyan 11 a ko wace shekara don ba da gudummawa da goyon baya ga sauran kasashe masu tasowa ta hanyar samar musu kayayyakin tsimin makamashi, don rage fitar da abubuwa masu gurbata muhalli, tare kuma da daga matsayinsu na tinkarar sauyin yanayi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China