in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya yi shawarwari da takwaransa na Congo Brazzaville
2014-06-12 20:34:30 cri

A Yau Alhamis 12 ga wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi shawarwari da takwaransa na jamhuriyar kasar Congo, Denis Sassou-N'guesso a nan birnin Beijing, inda Xi ya jaddada cewa, kamata ya yi a kara kokarin hadin gwiwa a fannonin man fetur, ba da lamuni, da kuma kwangiloli, da neman samun sabuwar hanyar hadin gwiwa, a kokarin sa kaimi ga kafa bankin da kasashen biyu suka suke zubawa jari, da ayyukan kafa hanyoyin jirgin kasa da tasoshin jirgin ruwa da na kasa don amfanin jama'ar kasar Congo Brazzaville..

Shugaba Xi ya jaddada cewa, Sin za ta yi kokarin kyautata dangantaka tsakaninta da kasashen Afirka, da nuna goyon baya ga kasashen Afirka da su daidaita matsalolinsu da kansu, da kara ba da gudummawa wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da bunkasuwar nahiyar Afirka. Dadin dadawa, Sin na fatan sa kaimi gainganta sabuwar dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakaninta da kasashen Afirka zuwa wani sabon mataki tare dabisa hadin kai da kasar Congo Brazzaville.

A nasa bangare, Shugaba Sassou-N'guesso ya bayyana cewa, Congo kasarsa na fatan karfafa hadin gwiwa tsakaninta da Sin, da sa kaimi ga jerin ayyukan hadin gwiwa, kuma tana maraba da zuwan kamfanonin Sin domin zuba jari a bangaren bunkasa albarkatun ma'adinai, da gina muhimman kayayyakin more rayuwar jama'a, da raya yankin musamman a fannin tattalin arziki. Congo na fatan karfafa mu'amala tsakaninta da Sin cikin a fannin harkokin MDD.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China