in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana na maraba da kamfanoni da masu zuba jari na kasar Sin
2015-03-27 20:52:06 cri

Minista mai kula da harkokin hanyoyin kasar Ghana Alhaji A.B.Inusah Huseini ya bayyana cewa, Ghana na maraba da kamfanonin kasar Sin da daidaikun mutune masu zuba jari na kasar da su shiga ayyukan gina manyan ababen more rayuwa da suka hada da hanyoyin mota, hanyoyin dogo da dai sauransu.

Yayin da yake zantawa da manema labaru a nan birning Beijing , Malam Huseini ya ce, ziyararsa kasar Sin a wannan karon na da nufin tabbatar da yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu a fannin kimiyya da fasaha ta fuskar tattalin arziki, da neman kyautata hanyoyin kasar ta samar da rancen kudi cikin gatanci. Ya kuma kara da cewa, yanzu gwamnatin kasar Ghana na tsara wasu manyan ababen more rayuwa ciki hadda hanyoyi masu saurin tafiya da sauransu, don hakan tana fatan masu zuba jari daga kasashen Sin Amurka da EU da sauransu su nuna himma da gwazo don shiga ayyukan gina wasu manyan ababen more rayuwa kamar su hanyoyin motoci da hanyoyin dogo, ita kuma a nata bangare, kasar ta Ghana zata samar da yanayi mai kyau ga masu zuba jari a wannan fanni. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Kasashen Sin da Ghana sun sanya hannu kan yarjejeniyar tsame wa juna amfani da Visa 2015-02-18 16:33:33
v Sin ta taimakawa kasar Ghana wajen raya sha'anin karatu daga gida 2015-02-03 10:54:44
v Gobara ta lalata wata cibiyar ajiye magunguna dake kasar Ghana 2015-01-14 14:48:54
v Masanan Sin sun isa kasar Ghana don fara horo ga likitocin kasar kan matakan rigakafi da yaki da cutar Ebola 2015-01-04 10:00:44
v Shugaban kasar Ghana ya bayyana kyakkyawan fata game da shiga sabuwar shekarar 2015 2015-01-01 16:08:43
v Kamfanonin Sin sun taimakawa jama'ar kasar Ghana wajen samun damar yin amfani da ruwa mai inganci 2014-12-24 15:15:50
v Ghana: An kada kuri'u a zaben shugabancin jam'iyyar NDC 2014-12-21 17:30:44
v An bude gasar wasannin nakasassu a Ghana 2014-12-13 16:50:48
v Kamfanin Sin zai ware dala miliyan 100 don kafa masana'antar kera motoci a Ghana 2014-09-15 14:29:31
v An kafa rukunin musamman a kasar Ghana don hana yaduwar cutar Ebola 2014-08-01 11:07:33
v Kamata ya yi shugabannin kasashen Afrika su koyi darussa daga kasar Sin 2014-07-02 15:56:34
v Ghana da Togo zusu kafa wata tashar binciken kan iyaka ta hadin gwiwa 2014-05-02 16:15:57
v An gayyaci Ghana halartar gasar U-17 ta kasashe 4 a Namibia 2014-04-09 15:54:21
v Sin za ta bayar da fasahar sinadarin uranium da ba shi da wani inganci sosai 2014-03-06 15:19:12
v Yawan ribar da Ghana ta samu daga zinariya da coco ta ragu 2014-02-14 15:52:47
v Kofi Annan ya yi kira da a gudanar da sauye sauye a tsarin zaben Ghana 2013-08-31 16:12:46
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China