in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana: An kada kuri'u a zaben shugabancin jam'iyyar NDC
2014-12-21 17:30:44 cri
Wakilan jam'iyyar NDC mai mulki a kasar Ghana, sun kada kuri'u, domin zaben sabbin shuwagabannin jam'iyyar. Sai dai rahotanni daga birnin Kumasi na cewa daya daga 'yan takarar kujerar shugabncin jam'iyyar, kuma magatakardar ta na farko Huudu Yahaya, ya janye daga zaben kafin fara kada kuri'un.

Sakamakon janyewar tasa, yanzu haka sakamakon zaben zai karkata ne ga ko dai shugaban jam'iyyar mai ci Kwabena Adjei, ko kuma babban jami'in hukumar kula da bala'u ta kasar Kofi Portuphy.

Kafin fara kada kuri'un dai sai da shugaban kasar ta Ghana John Dramani Mahama, ya ja hankalin wakilan jam'iyyar da su hada kai wuri guda, tare da magance rikicin cikin gida, dama kalubalen dake fuskantar jam'iyyar daga 'yan adawa. Ya ce hadin kan 'ya 'yan jam'iyyar ne kadai zai iya bata damar lashe zabubbuka, ta kuma samu zarafin ciyar da kasar gaba.

A halin yanzu dai jam'iyyar ta NDC ce ke rike da kujerun majalissar dokokin kasar 147 cikin 275, yayin da jam'iyyar adawa ta NPP ke da kujeru 121.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China