in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gobara ta lalata wata cibiyar ajiye magunguna dake kasar Ghana
2015-01-14 14:48:54 cri
Wata babbar gobara ta lalata wata cibiyar ajiye magunguna mai nisan kilomita 30 daga gabashin birnin Accra na kasar Ghana a ranar goma sha uku ga watan Janairu. Wani jami'in hukumar kiwon lafiya ta kasar ya bayyana cewa, a halin yanzu ba a ba da wani adadi game dahasarorin da wannan gobara ta haddasa,amma ana ganin gobarar zata iyar kawo babban illa ga magungunan rigakafi da bada jinya ga cutar Ebola dake wannan wurin.

An ce dai wannan gobara ta tashi da misalin karfe 9 na safe, sannan kuma a kwashe sa'o'i da dama kafin aka kashe wajen da yamma. Wani babban jami'in hukumar kashe gobara ta kasar Ghana ya bayyana cewa, watalika yanayin zafi da iska mai karfi na daga cikin dalilan haddasa wannan gobara.

Ministan kiwon lafiya na kasar Ghana KwakuAgyeman-Mensah ya bayyana cewa, ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar tana da isassun magunguna da za'a iyar yin amfani da su har zuwa tsawon watanni 3, don haka kadda jama'a su damu sosai dawannan lamarin.

An kafa hedkwatartawagar MDD ta musamman kan yaki da cutar Ebola a kasar Ghana, kana Ghana ita ce tashar zirga-zirga da kuma jigilar kayayyaki wajen yaki da cutar Ebola a yankin yammacin Afirka, kana cibiyar da gobara ta lalata ita ce ma'ajiyar magunguna mafi girma ta ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Ghana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China