in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamata ya yi shugabannin kasashen Afrika su koyi darussa daga kasar Sin
2014-07-02 15:56:34 cri

Shugabar jam'iyyar babban taron jama'ar kasar Ghana ta CPP Madam Samia Nkrumah ta bayyana cewa, ya kamata daukacin kasashen Afrika su koyi darussa daga kasar Sin wadda ta samu bunkasuwa cikin sauri.

Samia Nkrumah a zantawarta da manema labaru a ranar 1 ga wata ta ce, Ghana na bukatar bunkasa sana'ar kere-kere da daga karfin sarrafa kayayyaki ta yadda za a inganta karfin kasa na yin takara a duniya. Daukacin kasashe masu tasowa ciki hadda Ghana suna maida hankali a kan yadda tattalin arzikin kasar Sin ke bunkasuwa cikin sauri, kuma suna kokarin koyon abubuwa masu kyau daga kasar.

A ganin Samia Nkrumah, dalilin da ya sa Sin ta samu bunkasuwa mai kyau shi ne bin hanyar samun bunkasuwa da ta dogara da kanta bisa halin da Sin take ciki, abin da ya kamata jama'ar kasashen Afrika su yi koyi. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China