in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin da Ghana sun sanya hannu kan yarjejeniyar tsame wa juna amfani da Visa
2015-02-18 16:33:33 cri
A jiya ne kasashen Sin da Ghana suka sanya hannu kan yarjejeniyar rashin amfani da Visa don shiga kasashen juna ga jami'an diflomasiyan kasashen biyu.

Wannan yarjejeniya za ta baiwa masu rike da fasfon diflomasiya ko na gwamnatin wadannan kasashe iznin shiga ko fita daga kasashen biyu ko yada zango a yankunan kasashen nasu ba tare da takardar Visa ba.

Jakadar Sin a kasar Ghana Sun Baohong da mataimakin ministan harkokin waje da hadewar yankuna na kasar Ghana Kwesi Quartey ne suka sanya hannun kan wannan yarjejeniya a madadin kasashen nasu.

A jawabinta Jakada Sun ta ce, sanya hannu kan wannan yarjejeniya wata babbar nasara ce wajen saukaka musaya tsakanin al'ummomin kasashen biyu,baya ga karfafa hadin gwiwa da abokantaka tsakanin Sin da kasar ta Ghana.

Shi ma a jawabinsa Mr Quartey ya ce,wannan yarjejeniya za ta kara zurfafa tare da daidaita kyakkyawar dangantakar dake tsakanin Ghana da kasar Sin.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China