in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kafa rukunin musamman a kasar Ghana don hana yaduwar cutar Ebola
2014-08-01 11:07:33 cri

Gwamnatin kasar Ghana ta sanar a daren ranar 30 ga watan Yuli cewa, an kafa rukunin musamaman dake kunshe da ma'aikatan kiwon lafiya, da ta tsaron kasa, da ta harkokin cikin gida da ta watsa labaru ta kasar don hana yaduwar cutar Ebola.

Rukunin ya gudanar da taron manema labaru karo na farko a ranar 31 ga watan Yuli da safe, inda aka bayyana cewa, kasar Ghana za ta sa ido sosai kan cutar Ebola. Shugaban sashen sa ido kan cututtuka na hukumar kiwon lafiya ta kasar Ghana ya bayyana cewa, ya zuwa yanzu, akwai mutane 24 da ake ganin sun kamu da cutar Ebola a kasar, amma a karshe a gane ba haka ba ne.

Ministan kiwon lafiya na kasar Ghana Mensah ya bayyana cewa, kasarsa ta shirya kafa cibiyar rigakafi da bada jinya ga cutar Ebola, kuma ana bukatar dukkan asibitocin kasar da su bude dakin killatacce, ya yi bayanin cewa, an bude tsarin sa ido a birane 14 da mutanen waje suke shiga kasar Ghana don sa ido ga dukkan mutane da suka shiga kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China