in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kofi Annan ya yi kira da a gudanar da sauye sauye a tsarin zaben Ghana
2013-08-31 16:12:46 cri
Tsohon babban magatakardar MDD Kofi Annan, ya yi kira da a gudanar da sauye sauye ga tsarin zaben kasar Ghana, kwana guda bayan da babbar kotun kasar ta yi watsi da karar da dan takarar jam'iyyar adawa ta NPP Nana Akufo-Addo ya shigar gabanta, yana kalubalantar sahihancin sakamakon da ya baiwa shugaba John Dramani Mahama nasarar lashe babban zaben da ya gabata.

Wata sanarwar da aka rabawa manema labaru, ta ruwaito Annan na cewa wajibi ne a magance irin matsalolin da aka fuskanta yayin zaben da ya gabata, tare kuma da yin cikakken garambawul ga tsarin zaben kasar, domin samun karbabben zabe da kowa zai yi amana da shi.

Baya ga taya shugaba Mahama murnar samun nasara da tsohon magatakardar MDD ya yi, a hannu guda ya kuma yabawa babbar kotun kasar bisa kokarinta na tantance dukkanin bayanan da aka gabatar mata kafin yanke hukuncin shari'ar.

A ranar Alhamis din da ta gabata ne dai babbar kotun kasar ta Ghana ta sallami kasar da dan takara, da makarraban jam'iyyar adawa NPP suka shigar, ta kuma tabbatar da shugaba Mahama a matsayin halastaccen shugaban kasar ta Ghana, wanda kuma zai ja ragamar kasar zuwa wasu shekaru 4 masu zuwa. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China