in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guinea-Bissau ta rufe kan iyakarta da kasar Guinea sakamakon fargabar yaduwar cutar Ebola
2014-08-13 11:26:10 cri

Firaministan kasar Guinea Bissau, Domingos Simoes Pereira, ya dauki mataki na rufe kan iyakar kasarsa da kasar Guinea, inda barkewar cutar Ebola ya haddasa mutuwar mutane 370 a kasar.

Pereire ya ce gwamnatin Guinea Bissau, ta yanke hukuncin rufe bangaren kudanci da gabashin kan iyakar kasarta da Guinea, saboda wannan ita ce hanya mafi inganci, da zata haramta yaduwar cutar a kasarsa.

Hukumar lafiya ta duniya tace kawo yanzu barkewar cutar ta Ebola yayi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da dubu daya a kasashen Africa ta yamma tun daga farkon wannan shekarar da muke ciki.( Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China