in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An dage komawa manyan makarantu a Ghana saboda Ebola
2014-08-13 15:48:11 cri
Mataimakin minista a ma'aikar lafiya ta kasar Ghana Okudzeto Ablakwa ya bayyana dage lokacin komawa daukacin makarantun gaba da na sakandare mallakar gwamnatin kasar, sakamakon matakan da ake dauka na kare bullar cutar Ebola a kasar.

Mr. Ablakwa ya ce makarantun za su kasance a rufe, har ya zuwa lokacin da za a karfafa aikin tantance, da karfafa tsaron iyakokin kasar don hana shigar cutar.

Mataimakin ministan wanda ya bayyana hakan ta wata kafar radio dake birnin Accra, ya kara da cewa an samar da sahihin tsari na yiwa daliban kasashen Najeriya, da Liberia da na Saliyo masu karatu a kasar gwaji, kafin su shiga kasar.

Bugu da kari ya Ablakwa ya ce gwamnatin kasar ta na da shirin dakatar da gudanar da tarukan kasa da kasa da na al'umma, duka dai domin cimma burin da aka sanya gaba.

Daga nan sai ya tabbatar wa al'ummar kasar ta Ghana, shirin da gwamnati ke da shi, na tabbatar da kare yaduwar wannan cuta mai hadari ta Ebola a daukacin sassan kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China