in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An killace mutumin da ake zaton ya kamu da cutar Ebola a kasar Rwanda
2014-08-11 11:09:49 cri

Ma'aikatar lafiya a kasar Rwanda ta ce ta killace wani mutum guda, da ake tsammanin ya kamu da cutar nan ta Ebola a wani babban asibitin kasar.

Ma'aikatar lafiyar wadda ta bayyana hakan cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Lahadi, ta kara da cewa yanzu haka ana dakon sakamakon gwajin da aka yiwa maras lafiyan.

An dai ce mutumin dalibi ne a fannin aikin likita daga wata kasa ta Turai, shi ne kuma mutum na farko da ake ganin mai yiwuwa ya kamu da wannan cuta ta Ebola a kasar ta Rwanda, tun bullarta a wasu kasashen dake yammacin Afirka.

Gwamnatin kasar dai ta bukaci al'umma da su kwantar da hankulansu, su kuma kara kulawa, yayin da ma'aikatar lafiyar kasar ke ci gaba da daukar matakan hana barkewar cutar a kasar. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China