in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan Najeriyar da aka yiwa gwajin Ebola a Hong Kong ba ya dauke da cutar
2014-08-11 10:56:19 cri
Cibiyar kare lafiyar al'umma ta birnin Hong Kong, ta ce sakamakon gwajin da aka yiwa wani dan Najeriya da ake zaton na dauke da cutar nan ta Ebola, ya nuna cewa baya dauke da kwayoyin cutar.

Cibiyar ta ce an gudanar da bincike kan mutumin ne a asibitin Princess Margaret, kuma shi ne mutum na farko da aka zaci yana dauke da wannan cuta a kan hanyar sa ta zuwa Hong Kong, tun bayan da cutar ta barke a wasu kasashen yammacin Afirka.

An ce mutumin dan shekaru 32 da haihuwa ya nuna alamun cutar ta hanyar amai da gudawa, ya kuma isa Hong Kong a ranar Alhamis. Inda daga nan aka aike da shi zuwa asibiti.

Mutane sama da 900 ne dai suka rasa rayukan su bayan sun kamu da cutar ta Ebola a wasu kasashen dake yammacin Afirka.

Tuni kuma hukumar lafiya ta WHO ta ayyana wannan cuta a matsayin wata annoba ga duniya baki daya, wadda kuma duniya ba ta gamu da kamar ta ba cikin shekaru 40 da suka gabata.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China