in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta nada Nabarro a matsayin mai lura da batutuwan da suka shafi cutar Ebola na majalissar
2014-08-13 14:32:19 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon ya bayyana nadin David Nabarro, a matsayin mai lura da batutuwan da suka jibanci cutar Ebola na MDD. Aikin da ake sa ran zai taimaka wajen cimma nasarar hana yaduwar cutar ta Ebola.

Ban Ki-moon ya bayyana hakan ne a gun taron manema labaru da aka gudanar a cibiyar MDD a jiya Talata. Ya kuma ce hadin kai tsakanin kasa da kasa domin shawo kan wannan cuta yana da muhimmancin gaske wajen tinkarar ta.

Nadin Nabarro dai ya biyo bayan ganawar da Mr. Ban ya yi da babbar direktar hukumar WHO Margaret Chan. Nabarro dai masani ne a fannin harkokin kiwon lafiya na WHO, ya kuma taba zama jami'i mai kula da cutar murar tsuntsaye na MDD.

Yayin tabbatar da nadin nasa, Mr. Ban Ki-moon ya kara da cewa, aikin farko da ake fatan zai gudanar shi ne, warware matsalar rashin karfin ikon tinkarar cutar da kasashen Guinea, da Liberia da Saliyo ke fuskanta, duba da cewa kasashen ba su jima da farfadowa daga rikice-rikicen siyasa ba.

Kaza lika Ban Ki-moon ya yi kira ga kasashen duniya, da su bada tasu gudummawa game da matsalar rashin isassun likitoci, da tufaffin bada kariya, da tantuna da sauran na'urori da ake bukata a wadannan kasashe, yana mai cewa kamata ya yi jama'a su yi watsi da tsoron cutar ta Ebola. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China