in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na kasar Sin ya gana da babban sakataren AL
2014-08-04 20:34:25 cri
Firaministan kasar Sin Wang Yi ya gana da babban sakataren kungiyar kawancen kasashen Larabawa AL Nabil el-Araby a jiya Lahadi 3 ga wata a hedkwatar ta dake birnin Alkahira.

A lokacin ganawar Wang Yi ya bayyana cewa, a kokarin da bangarorin biyu suke yi, taron ministoci karo na shida na dandalin tattaunawar hadin kai tsakanin Sin da kasashen Larabawa ya samu ci gaba sosai saboda a taron shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tsai da shirin da bangarorin biyu za su bi wajen yin hadin gwiwa da hanyar da za a bi nan gaba. Ministan yace wannan ya baiwa dangantakar dake tsakanin bangarorin biyu makoma mai kyau a cikin shekaru 10 masu zuwa. Don haka in ji shi ya kamata, bangarorin biyu sun dauki matakai da suka dace domin tabbatar da ci gaban da aka samu a taron.

A nashi bangare, Nabil el-Araby ya lura da cewa, Sin ta kan bin hanyar adalci da daidaici, kuma tana goyon bayan ayyuka masu kyau da kasashen Larabawa suke yi, abin da ya nuna cewa, Sin sahihiyar abokiya ce ga kasashen Larabawa wadda suke iya dogaro da ita. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Hamas ta nuna shakku game da batun tsagaita bude wuta da Isra'ila ta sanar 2014-08-04 10:51:26
v Ma'aikatar wajen Amurka ta nuna takaici game da harin da Isra'ila ta kai a kusa da makarantar MDD 2014-08-04 10:44:33
v Ban Ki-moon ya yi tir da harin da Isra'ila ta kai a kusa da makarantar MDD a Gaza 2014-08-04 10:43:19
v Shugaban Falesdinu zai je birnin Alkahira don tattauna batun tsagaita bude wuta a yankin Gaza 2014-08-02 16:41:17
v Sojojin Isra'ila sun bayyana kawo karshen wa'adin tsagaita bude wuta da suka cimma da Hamas 2014-08-01 20:26:35
v An sake kai harin boma-bomai a yankin Gaza bayan dokar tsagaita bude wuta ta fara aiki 2014-08-01 20:20:45
v Mutane fiye da dubu 9 sun mutu ko raunata a sakamakon rikicin Palesdinu da Isra'ila 2014-08-01 10:36:43
v Ana ci gaba da musayar wuta tsakanin Palesdinu da Isra'ila 2014-07-31 10:47:59
v Wakilin MDD ya jinjinawa shawarar kafa sabuwar jihar tsakiyar Somalia 2014-07-31 10:01:10
v Mayakan Izz el-Deenal-Qassam sun yi watsi da sabon kudurin tsagaita bude wuta 2014-07-30 14:50:29
v An kawo karshen yarjejeniyar tsagaita bude wuta tsakanin Palesdinu da Isra'ila 2014-07-29 14:26:04
v Kwamitin tsaron MDD ya yi kira da a fidda sahihin tsarin aiwatar da sulhu a Mali 2014-07-29 09:57:16
v Ministan harkokin wajen Sin ya gana da sakatare janar na kungiyar AL 2014-01-24 10:54:27
v Rasha ta ki yarda da baiwa kungiyar adawa da gwamnatin kasar Sham matsayin mambar kungiyar kasashen duniya 2013-03-29 15:15:17
v AL ta ba da damar kasance mambarta ga kungiyar 'yan adawar Syria 2013-03-27 14:52:32
v Kungiyar tarayyar kasashen Larabawa ta bude taro a Doha da nufin duba rikicin Sham 2013-03-26 20:06:14
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China