in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane fiye da dubu 9 sun mutu ko raunata a sakamakon rikicin Palesdinu da Isra'ila
2014-08-01 10:36:43 cri
Yawan mutane da suka mutu ko raunata a sakamakon rikicin tsakanin Palesdinu da Isra'ila na tsawon makwanni fiye da uku ya ci gaba da karuwa, ya zuwa yanzu yawansu ya zarce dubu 9. Kana MDD ta bayyana cewa, mutane dubu 440 sun rasa gidajensu a zirin Gaza, don haka ana fuskantar halin jin kai mai tsanani.

Bisa kididdigar da Palesdinu ta yi, an ce, mutane a kalla 1422 ne suka mutu a sakamakon aikin soja da Isra'ila ta dauka a zirin Gaza, kana mutane fiye da 7800 sun ji rauni, kuma yawancinsu fararen hula ne. Yawan mutanen da suka mutu ko raunata ya karu sosai a sakamakon ruwan boma-bomai da sojojin Isra'ila suka yi a kwanakin baya.

Kwamitin sulhu na MDD ya gudanar da taro cikin gaggawa game da hali mai tsanani a zirin Gaza da aka kai hare-hare ga sansanin 'yan gudun hijira na MDD dake zirin Gaza, inda mataimakiyar babban sakatare mai kula da harkokin jin kai na MDD Valerie Amos ta yi bayani cewa, yanzu babu inda ake da zaman lafiya a zirin Gaza.

Hakazalika kuma Amos ta bayyana cewa, a halin yanzu mutane fiye da dubu 440 sun rasa gidajensu, wanda ya kai kashi 24 cikin dari na yawan mutane a zirin Gaza. Mutane dubu 240 a cikinsu sun zabi kaura zuwa sansanin 'yan gudun hijira na MDD dake dab da sashen bada taimako ga 'yan gudun hijira a gabashin Palesdinu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China