in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar tarayyar kasashen Larabawa ta bude taro a Doha da nufin duba rikicin Sham
2013-03-26 20:06:14 cri
An bude taron kungiyar tarayyar kasashen Larabawa karo na 24 a birnin Doha na kasar Qatar da babban makasudin duba yanayin da ake ciki a kasar Sham cikin jadawalinsa.

Taron da ya samu halarta a kalla shugabannin kasashen Larabawa 15 sun hada da shugaban kasar Masar Mohamed Morsi, sarkin Qatar Sheikh Hamad bin Khalifa Al-Thani da kuma shugaban al'ummar Palestinu Mahmoud Abbas.

Moaz al-Khatib, shugaban kungiyar 'yan adawa na kasar Sham mazauna kasashen waje da ya yi murabus shi ne ya zauna a kan kujerar wakilin Damascus, kuma ana sa ran zai gabatar da jawabinsa a lokacin wannan taro.

Shi dai wannan taro na kwanaki biyu shi ne na 24 tun kafuwar kungiyar, wanda a da ake kiran shi gamayyar kasashen Larabawa lokacin da aka kafa shi a shekarar 1945.

Mataimakin shugaban kasar Iraqi Khudeir Musa Al Khuza tun da farko a cikin jawabinsa ya yi kira ga kungiyar da ta kafa wani kwamitin tsaro da zai warware wannan matsala da ake fuskanta na tashin hankali a kasar ta Sham.(Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China