in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Falesdinu zai je birnin Alkahira don tattauna batun tsagaita bude wuta a yankin Gaza
2014-08-02 16:41:17 cri
An sake yin musayar wuta a yankin Gaza a ran 1 ga watan Agusta bayan Falesdinu da Isra'ila suka cimma matsayi daya kan tsagaita bude wuta na sa'o'i 72 a ran 31 ga watan Yuli, lamarin ya haddasa mutuwar Falesdinawa da dama. Sa'nan nan, bangarorin biyu sun sanar da kawo karshen wa'adin tsagaita bude wuta. Don gane haka, shugaban Falesdinu Mahmoud Abbas ya bayyana a jiya Jumm'a cewa, zai je birnin Alkahira tare da tawagar wakilan kasar don yin tattaunawa kan yarjejeniyar tsagaita bude wuta a yankin Gaza a ran 2 ga wata.

Bugu da kari, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya ba da wata sanarwa a ran 1 ga wata cewa, take yarjejeniyar tsagaita bude wuta a yankin Gaza ta bata masa rai sosai, don haka, ya yi alla wadai da dukkanin matakan da aka dauka wadanda suka janyo rashin girmama yarjejeniyar da aka cimma, ya kuma yi kira ga Falesdinu da Isra'ila da su dukufa wajen kai zuciya nesa, a sake dawo yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta sa'o' i 72 da aka kulla a baya, ya kuma yi kira ga bangarorin daban daban na gamayyar kasa da kasa da su ba da taimako wajen ciyar da tsagaita bude wuta a yankin Gaza gaba.

Haka zalika, shugaban kasar Amurka Barack Obama ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, Amurka ta yi allawadai da farmakin da dakarun Falesdinu suka kai kan sojojin Isra'ila bayan fara aikin yarjejeniyar tsagaita bude wuta a wannan rana. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China