in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jaddada wajibacin raya karfin rundunar soja domin tabbatar da zaman karko da kwanciyar hankali
2014-05-02 16:32:55 cri

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika gaisuwa ga rundunar sojan da aka girke a jihar Xinjiang, yayin da ya kai musu ziyara daga ran 27 zuwa 29 ga watan Afrilu da ya gabata, inda kuma ya nazarci yadda za a gudanar da aikin kiyaye zaman karko da kare rayuka da dukiyoyin jama'a. Ban da haka kuma a madadin kwamitin tsakiyar na jam'iyyar Kwaminis ta Sin da majalisar gudanarwa da rundunar sojan kasar, ya mikawa daukacin jami'an soja da wadanda suka shirya shiga soja gaisuwa. Inda Mr Xi ya jaddada cewa, ya kamata a cimma burin JKS na karfafa sojojin kasar, ta yadda za a kare martabar su a dukkan fannoni domin ba da tabbaci ga zaman karko da kwanciyar hankali cikin dogon lokaci a jihar Xinjiang. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China