in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane uku sun mutu sakamakon harin ta'addanci da aka kai a Xinjiang
2014-05-01 16:23:33 cri
Wani bam din da ya tashi a tashar jiragen kasan birnin Urumqi na jihar Xinjiang a ran 30 ga watan Afrilu da misali karfe 7 na yamma, ya yi sanadin mutuwar mutane 3, yayin da wasu 79 suka raunana, 4 daga cikinsu sun samu munanan raunuka.

Yayin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya samu wannan labari, nan da nan ya ba da umurnin daukar matakin da ya dace wanda za a kwashe dogon lokaci domin gudanar da shi, haka kuma ya kamata a ba shi muhimmanci sosai. A cewar shugaban kamata ya yi, jihar Xinjiang mai cin gashin kanta ta ba da kulawa da wadanda suka raunana cikin lokaci da bincike kan al'amari ta yadda za a yanke hukunci ga wadanda suka aikata laifin yadda ya kamata. Kamata ya yi, a kwantar da hankulan jama'a da ba da tabbaci ga kare lafiyar jama'a da dukiyoyinsu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China