in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka za ta garkamawa wadanda suka rura wutar rikicin kasar Afrika ta tsakiya takunkumi
2014-01-28 16:40:24 cri
Ministan harkokin wajen kasar Amurka, John Kerry ya bayyana a jiya Litinin 27 ga wata cewa, Amurka ta yi shirin garkamawa wadanda suka rura wutar rikicin dake cigaba da tsanantawa a kasar Afrika ta tsakiya takunkumi.

A cikin wata sanarwar da ya bayar, mista Kerry ya bayyana cewa, sun samu bayanan dake nuna cewa akwai wasu shugabannin kasar dake rufe ido game da yunkurin farfado da zaman lafiya, a maimakon haka, suna cigaba da nuna goyon baya ga wasu mayaka domin kara zafafa wutar rikici, lamarin dake daukar hankalin gwamnatin kasar Amurka kwarai.

Bugu da kari, Kerry ya kalubalanci shugabar wucin gadin kasar da tsoffin shugabannin kasar da su yi kira ga magoyansu da su daina kai hare hare ko amfani da karfin tuwo kan fararen hula. Ban da haka, ya yi kira ga kasashe makwabta da su daina taimakawa dakarun kasar Afrika ta tsakiya da makamai da makamantan haka. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Yawan sojin da kasar Faransa za ta tura Afrika ta tsakiya zai kai 1600, in ji shguaban Faransa 2013-12-08 16:56:09
v Sojojin Faransa sun isa birnin Bangui hedkwatar Afrika ta tsakiya 2013-11-29 16:38:20
v Rikici a kasar Afrika ta tsakiya ya haddasa mutuwar mutane 50 2013-10-09 16:44:58
v Kungiyar LRA a kasar Afrika ta tsakiya ta amince da kwance damara 2013-09-23 14:18:40
v Faransa ta nemi a kafa sabuwar gwamnatin Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya bisa doka 2013-04-18 11:13:00
v MDD ta yi gargadi kan halin da ake ciki a kasar Afrika ta tsakiya dangane da isashen hatsi 2013-02-16 16:32:08
v MDD ta bayar da rahoton kwasar ganima da wawushe kauyuka a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya 2013-02-13 16:26:53
v MDD ta yi maraba da kafuwar sabuwar gwamnati a kasar Afirka ta Tsakiya. 2013-02-06 10:47:58
v Kwamitin sulhu na MDD ya tsawaita lokacin aikin kafa zaman lafiya a CAR na shekara daya 2013-01-25 11:16:29
v Kasar Sin tana fatan taimakawa Afrika ta tsakiya don cimma burin tabbatar da zaman lafiya da karko 2013-01-15 16:55:02
v An tube firaministan Afirka ta Tsakiya daga mukaminsa 2013-01-13 16:42:39
v Shugaban kasar Afirka ta Tsakiya ya cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta tare da 'yan adawa 2013-01-12 17:10:54
v Shawarwari kan warware rikicin Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ya shiga halin kila-wa-kila 2013-01-10 16:49:21
v Faransa na fatan bangarori daban-daban na Afrika ta tsakiya za su yi shawarwari tun da wuri 2013-01-08 14:06:47
v Bai kamata a warware rikicin kasar Afirka ta tsakiya ta hanyar matakan soja ba, a cewar kwamitin sulhu na MDD 2013-01-05 16:22:37
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China