in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi gargadi kan halin da ake ciki a kasar Afrika ta tsakiya dangane da isashen hatsi
2013-02-16 16:32:08 cri
Hukumar tsara shirin abinci ta duniya ta MDD wato WFP ta yi gargadi a ran Juma'a 15 ga wata cewa, kasar Afrika ta tsakiya za ta fuskanci matsalar rashin samun isashen hatsi sakamakon rikicin siyasa da na soja da take fama da su.

Bisa kiyashi da MDD da ma wasu hukumomi masu zaman kansu suka yi, an ce, tun lokacin da aka dakatar da aikin ciniki daga watan Disamba na shekarar bara tsakanin yankin da kungiyar adawa ta Seleka ta mallaka da sauran wurare, aka samu hauhawar farashi, bisa kalaman kakakin MDD Martin Nesirky yayin taron manema labaru a wannan rana.

WFP ta nuna cewa, kwasar ganima da aka yi a wannan wuri ya haddasa koma baya waje samar da kayayyaki, da kuma abinci, da ma wasu kayayyakin gona da dabbobi, ga kuma fargaba da manoma ke yi inda hakan ya hana su gudanar da aikinsu.

Bugu da kari WFP ta ce, yawan abinci da ake bukata ya karu da kashi 40 bisa dari a wurare dake karkashin sojin kasar. Amma, a cewar Nesirky, wasu wuraren dake karkashin Seleka na fama da karancin abinci saboda hauhawar farashin, inda hakan ya kawo illa ga mutane fiye da dubu 800 a wadannan wurare. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China