in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tana fatan taimakawa Afrika ta tsakiya don cimma burin tabbatar da zaman lafiya da karko
2013-01-15 16:55:02 cri
A ranar 15 ga wata, a gun taron manema labarun da aka saba yi, kakakin ma'aikatar kula da harkokin wajen kasar Sin Hong Lei ya bayyana cewa, Sin ta mai da hankali sosai game da yanayin da ake ciki a kasar Afrika ta tsakiya, kuma ta yi la'akari da sakamakon shawarwari da aka cimma a birnin Libreville hedkwatar kasar Gabon da yarjejeniyoyin da aka daddale tsakaninsu, matakin da ya aza wani harsashin warware rikicin kasar, kuma kasar Sin ta yi maraba da wannan.

Rikici yaki-ci-yaki-cinyewa a tsakanin gwamnatin kasar Afrika ta tsakiya da dakarun da ke adawa da gwamnatin har tsawon sama da wata guda, kuma a karkashin shiga tsakani da kungiyar AU da kungiyar raya tattalin arziki na kasashen yankunan tsakiyar Afrika da kasashen da abin ya shafa suka yi, a ranar 11 ga wata, bangarorin da rikicin Afrika ta tsakiya ya shafa sun daddale yarjejeniyar tsagaita bude wuta cikin wata sanarwa, kana da yarjejeniyoyin siyasa tsakaninsu.

Hong Lei ya ce, kasar Sin tana fatan bangarorin da abin ya shafa za su dauki hakikanin mataki don aiwatar da yarjejeniyar da aka daddale tsakaninsu, don sa kasar ga alkiblar samun bunkasuwa yadda ya kamata, kuma kasar Sin tana fatan yin kokari tare da kasashen duniya, don ci gaba da taimakawa Afrika ta tsakiya wajen cimma dauwamammen zaman lafiya da na karko. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China