in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Faransa sun isa birnin Bangui hedkwatar Afrika ta tsakiya
2013-11-29 16:38:20 cri
Kafofin yada labaru na kasar Faransa sun bayyana a ran 28 ga wata cewa, sojojin Faransa da suka yi shirin shiga tsakani a jamhuriyar Afrika ta tsakiya, suna ta jigilar sojoji da makamai zuwa birnin Bangui hedkwatar Afrika ta tsakiya daga kasashen da ke makwabtaka da ita.

Rahotanni sun ruwaito bangaren soji na Afrika ta tsakiya na cewa, a ranar 28 ga wata, wasu jiragen saman yaki sun yi jigilar sojoji da makamai daga kasar Gabon zuwa birnin Bangui. Ban da wannan kuma, motocin sojojin Faransa dake sintiri da motoci masu sulke sun tashi daga kasar Kamaru don shiga Jamhuriyar Afrika ta tsakiya.

A ranar 27 ga wata, shugaban kasar Faransa François Hollande ya fada wa kafofin yada labaru cewa, kasashen duniya ba za su amince yanayin jin kai da ake ciki a jamhuriyar Afrika ta tsakiya ya ci gaba da tabarbarewa ba, kuma hakkin Afrika ta tsakiya ne ta sauke nauyin da ke wuyansa game da halin da ake ciki a kasar.

Kwanan baya, dakarun Seleka gabilin su Musulmai da wasu dakarun tsaron kai na kananan hukumomin kasar galibinsu kiristoci sun yi artabu a tsakaninsu, abin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane kimanin 100, tare da haddasa tabarbarewar al'amura.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China