in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rikici a kasar Afrika ta tsakiya ya haddasa mutuwar mutane 50
2013-10-09 16:44:58 cri
A ranar 8 ga wata, an yi rikici a wani kauyen da ke yankin arewa maso yammacin kasar Afrika ta tsakiya da ya yi sanadiyyar mutuwar a kalla mutane 50, tare da jikkatar wasu fiye da 10, kuma bangarorin biyu da rikicin ya shafa su ne, tsohon kawacen dakarun dake adawa da gwamnati wato Séléka da rundunar sojoji masu tsaron kai na kananan hukumomin kasar.

Wani mutum da ke da alaka da manyan jami'an soji da ke birnin Bangui hedkwatar Afrika ta tsakiya ya bayyana cewa, a ranar 7 ga wata, rundunar sojoji masu tsaro kai ta kananan hukumomin kasar sun fara kai farmaki ga wani kauyen da ke yankin arewa maso yammacin kasar, kuma abin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 3, tare da jikkatar wasu sama da 10, daga bisani kuma, kawacen dakarun Seleka sun fatatake su. Ya zuwa ranar 8 ga wata da safe, ana ci gaba da rikici a tsakaninsu, kuma abin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane a kalla 50. haka kuma, mazaunan kauyen sun riga sun bar kauyensu, kuma sun buya a gandun daji.

Kwanan nan, dakarun Seleka da ke bin addinin musulunci da rundunar sojojin tsaron kai ta kananan hukumomin kasar masu bin addinin kirista sun kara yin rikici mai tsanani a tsakaninsu.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China