in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan sojin da kasar Faransa za ta tura Afrika ta tsakiya zai kai 1600, in ji shguaban Faransa
2013-12-08 16:56:09 cri
Yawan sojin da kasar Faransa za ta tura a Afrika ta tsakiya zai kai 1600 zuwa daren Asabar 7 ga wata, shugaban kasar Faransa Francois Hollande ya yi wannan furici a ranar a birnin Paris na kasar Faransa. Yana mai cewa, babban aikin sojin kasar shi ne kawar da dakarun sojojin sa kai da kungiyoyin masu fafutuka dake afkawa fararen hula.

Bisa labarin da kafar yada labaru ta kasar ta bayar an ce, ya zuwa yanzu, sojoji 1200 sun kama aikinsu yadda ya kamata, kuma sun fara yin sintiri a birnin Bangui hedkwar kasar ta Afrika ta tsakiya da ma sauran muhimman wurare. An ce, a ranar 5 ga wata sojojin Faransa ya mayar da martani ga masu dauke da makamai dake kokarin kai hari kan fararen hula da jami'an tsaro na Faransa a kusa da filin saukar jiragen sama dake Bangui.

Ministan tsaron kasar Faransa Jean Yves Le Drian ya sanar a ran 6 ga wata cewa, Faransa ta riga ta fara ayyukanta a Afrika ta tsakiya da za su shafe tsawon watanni shida, da zummar farfado da tsaron kasar, tare kuma da ba da taimako wajen jibge rundunar sojojin kasashen Afrika da dama. Wannan ya kasance matakin soja na biyu da Faransa take dauka a wannan shekara a Afrika. An ce, bisa rokon gwamnatin kasar Mali a watan Janairun shekarar bana, Faransa ta tura sojinta zuwa kasar ta Mali dake yammacin Afrika domin taimawa kasar dakile masu tsatsaurancin ra'ayi kishin islama dake arewacin kasar. Har ila yau, sojojin Faransa na cigaba da fafatawa a kasar Mali tare da masu fafutuka. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China