in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bayar da rahoton kwasar ganima da wawushe kauyuka a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya
2013-02-13 16:26:53 cri
Mai Magana ya yawun MDD ya fada a ranar Talata cewa, tawagar da ke kimanta ayyukan jin kai da hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD ta taru Bambari da ke Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya a makon da ya gabata, ta ga yadda ake ta kwasar ganima tare da wawushe kauyuka.

Kakakin MDD Martin Nesirky ya fada yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa a ko wace rana cewa, "tawagogin hadin gwiwar da MDD ta rura, sun ga yadda ake ta kwasar ganima da wawushe kauyukan da ke tsakanin Grimari da Bambari mai nisan kilomita 100, inda mazauna yankunan ke buya a cikin daji".

Ya ce wannan tawaga ita ce ta farko da aka tura shiyyar, tun tsakiyar watan Disamba, lokacin da gamayyar 'yan tawayen Seleka suka kwace manyan biranen da ke arewaci da tsakiyar kasar, ciki har da Bambari da Kaga Bandoro.

'Yan tawayen dai sun kwace kusan kashi 1 bisa 3 na kasar ne kafin yarjejeniyar zaman lafiya da aka sanyawa hannu a ranar 11 ga watan Janairu a Libreville, babban birnin kasar Gabon.

Don haka, ya ce hukumar ta bukaci 'yan tawayen na Seleka da gwamnati, da su bari ma'aikatan agaji su kai dauki ga al'ummomin da ke bukatar taimako, a kasar da aka yi kiyasin mutane 80,000 rikici ya wargaza, baya ga karin 'yan gudun hijira 17,000 daga Sudan. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China