in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi maraba da kafuwar sabuwar gwamnati a kasar Afirka ta Tsakiya.
2013-02-06 10:47:58 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayyana amincewarsa da kafuwar gwamnatin hadaka a kasar Afirka ta Tsakiya, yana mai cewa, hakan wani kyakkyawan mataki ne na karfafa zaman lafiya da lumana a kasar.

Wani kudurin doka dake dauke da sa hannun shugaba Francois Bozize da fadar gwamnatin kasar ta fitar a ranar Lahadin da ta gabata ya bayyana sunan Michel Dotodjia Am Nondroko dake matsayin shugaban kungiyar 'yan tawayen Seleka, a matsayin mataimakin firaminista, kuma ministan tsaron gwamnatin wucin gadin kasar.

Kafuwar wannan tsari na gwamnatin hadaka dai a kasar ta Afirka ta Tsakiya ya zo bayan shafe tsawon lokaci ana tattaunawa tsakanin gwamnatin da 'yan tawaye, inda daga karshe yarjejeniyar da aka cimma a Libreville ta tanadi kafa gwamnatin rikon kwarya da za a rika sabuntawa bayan shekara guda, yayin da kuma ake sa ran gudanar da zaben 'yan majalisar kasar a shekara mai zuwa.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China