in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fitar da rukunai na gasar cin kofin duniya da za'a shirya a Brazil
2013-12-08 19:54:48 cri
An gabatar da sakamkon jefa kuri'a na rukuni rukuni na gasar cin kofin duniya a Brazil a jiya Asabar 7 ga wata. A cikin kungiyoyin da suka fito daga nahiyar Afrika, kasar Najeriya na daga cikin kasashen mafi karfi a cikin rukuninta na F, dalilin haka ake ganin Najeriya nada makoma mai haske, a yayin da kasar Ghana ta samu kanta cikin rukunin G mai wuya da ya hada da manyan kasashen kwalon kafa.

Kungiyar Nijeriya da ake yi ma lakabin "juruma ta Afrika" ta taki sa'a domin tana cikin rukunin da babu kungiyoyi masu karfi da yawa baya ga Argentina wanda Nijeriya ta taba yin gasa tare da shi a cikin gasar cin kofin duniya a Afrika ta kudu, sannan kungiyar Bosnia ba ta taba halartar babbar gasar a baya ba, a nata bangaren kuma kungiyar Iran daga nahiyar Asiya ta samu koma baya sosai a shekarun baya-baya, abubuwan da da ake gani za su baiwa kungiyar Nijeriya damar cimma nasara a rukunin da take ciki.

Ban da haka, kungiyar Cote D'ivoire a karkashin jagorancin Drogba da kungiya daya kawai daga arewacin Afrika Aljeriya su ma suka sami sa'a. Cote D'ivoire ba za ta tinkarar 'yan takara masu karfi ba a cikin kungiya ta C, ganin Columbia, Greek, da Japan, ba su da karfi sosai idan an kwatanta su da Cote d'ivoire wadda ake mata lakabin babbar giwar Afirka. A bangare na daban, Aljeriya zai fuskanci Bulgium, Rasha da Korea ta kudu, wadanda su ma ba su da karfi sosai. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Majalisar dattawan Najeriya za ta yi bikin nasarar kofin da matasa 'yan kasa da shekaru 17 suka lashe 2013-11-13 10:11:11
v Nijeriya ta lashe gasar cin kofin duniya ta U17 2013-11-09 15:46:53
v Kungiyar wasan kwallon kafa ta Nijeriya ta cimma nasarar shiga gasar cin kofin duniya ta shekarar 2014 2013-09-08 17:08:57
v Kasar Morocco ta doke Tunusiya a wasan share fagen shiga gasar zakarun kwallo kafa ta nahiyar Afirka (CHAN) 2013-07-19 16:54:33
v An yi bikin tunawa da 'yan wasan kwallon kafan Zambia da suka mutu sanadiyar hadarin jirgin sama shekaru 20 da suka wuce 2013-04-29 17:00:44
v Najeriya za ta sake hado 'yan wasa da za su buga wasan fidda masu zuwa gasar cin kofin duniya 2013-03-01 10:33:14
v Kasar Ghana za ta gudanar da tsarin tushe na wasan kwallon kafa na hukumar FIFA 2012-04-20 15:29:57
v Yan wasan kwallon kafa na kasar Kamaru zasu taka gasar sada zumunci tare dana takwarorinsu na kasashen Burkina-Faso da Nijar 2012-01-10 16:35:35
v Moussa Sow aka zaba zakaran "Ballon d'Or" na shekarar 2011 na kasar Senegal 2011-12-27 11:27:31
v Hukumar kwallon kafa ta Zimbabwe ta tsara sabon kundi 2011-11-04 10:50:00
v Hukumar kwallon kafa ta Afirka ta kudu ta kai kara bayan da kungiyar ta kasa kaiwa ga shiga gasar cin kofin kwallon kafa na nahiyar Afirka 2011-10-10 10:22:56
v Kasar Tanzania za ta karbi bakuncin wasan cin kofin kalubale na yankunan gabashin da tsakiyar Afrika 2011-09-29 15:07:36
v Shugaban kwamitin tsaro na hukumar FIFA ya bukaci kasar Zimbabwe da ta dakatar da akidar sayen wasa 2011-09-26 10:54:48
v An karrama 'yan wsan kwallon kafa na kasar Ghana da lambar wasanni ta nahiyar Afrika 2011-09-23 15:06:27
v Kasar Afrika ta Kudu ta ragu da mataki hudu a fagen kwallon kafa 2011-09-22 14:48:13
v Za'a shirya wasan kwallon kafar sada zumunci tsakanin jamhuriyar demokaradiyar Congo da kasar Angola 2011-08-23 10:31:25
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China