in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta lashe gasar cin kofin duniya ta U17
2013-11-09 15:46:53 cri
An kammala wasan karshe na gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya a matsayin 'yan kasa da shekaru 17 na bana a jiya juma'a a kasar hadaddiyar daular Larabawa, inda kungiyar kwallon kafar Nijeriya ta lashe ta kasar Mexico da ci uku da nema, matakin da ya baiwa kungiyar damar daukar kofin na bana a karo na 4.

An yi wasan karshe ne dai a filin wasa na Mohammad Bin Zayed dake birnin Abu Dhabi na kasar hadaddiyar daulolin Larabawa, inda Nijeriya ta doke kasar Mexico wadda ke rike da kambin gasar a karon da ya gabata. Daukar kofin a karo na hudu da Nijeriya ta yi ya karya matsayin bajimtar da kungiyar kasar Brazil ta kafa, na zama zakara sau uku a gasar.

Dama dai, kafin wasan karshen, sai da kungiyar Sweden ta lashe ta Argentina da ci hudu da daya. Wanda hakan ya sanya Sweden din zama a matsayi na uku, yayin da kuma Argentina ta ke a matsayi na hudu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China