in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dattawan Najeriya za ta yi bikin nasarar kofin da matasa 'yan kasa da shekaru 17 suka lashe
2013-11-13 10:11:11 cri

A ranar Talata ne majalisar dattawan Najeriya, ta amince da wani kuduri, don karrama 'yan wasan Golden Eaglets da masu horas da su sakamakon nasarar da suka yi ta lashe kofin kwallon kafa na duniya na 'yan kasa da shekaru 17.

Majalisar ta amince da kudurin ne domin taya Najeriya murnar nasarar da 'yan wasan na Golden Eaglets suka yi a gasar, wadda aka gudanar a hadaddiyar daular kasashen Larabawa.

Shugaban kwamitin wasanni na majalisar dattawan Najeriya, Senata Adamu Gumba ne ya gabatar da kudurin wanda ya samu amincewar dukkan sanatocin.

Majalisar ta kuma taya 'yan wasan, masu horas da su da baki dayan 'yan Najeriya saboda kishi da hadin kan da suka nuna a lokacin gasar wadanda suka ba su nasarar lashe wannan kofi na karo na hudu. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China