in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar wasan kwallon kafa ta Nijeriya ta cimma nasarar shiga gasar cin kofin duniya ta shekarar 2014
2013-09-08 17:08:57 cri
A ranar 7 ga wata a filin wasa na Calabar na kasar Nijeriya, kungiyar wasan kwallon kafa ta kasar Nijeriya ta lashe kungiyar Malawi da cin biyu da ba ko daya a gasar rukunin neman shigar gasar cin kofin duniya ta kasar Brazil a shekarar 2014 a zagaye na farko a yankin Afirka. Don haka, kungiyar kasar Nijeriya ta samu maki 12 da kasancewa ta farko a rukunin F, da shiga gasar a tsakanin kungiyoyi 10 don neman samun iznin shiga gasar cin kofin duniya ta 2014.

A gasar zagayen farko ta yankin Afirka ta neman shiga gasar cin kofin duniya a wannan karo, kungiyar kasar Nijeriya, Malawi, Namibia da kuma Kenya suke cikin rukunin F. Bayan gasanni 5 a tsakaninsu, kungiyar kasar Nijeriya ta samu maki 9 da cimma nasarar gasa sau biyu da kuma yin kunnen doki sau uku. Yin kunnen doki a gasa ta karshe ya iya taimaki kungiyar Nijeriya wajen shiga zagaye na gaba.

Bayan da kungiyar Nijeriya ta samu nasara karawarta tare da kasar Malawi, ta samu maki 12 da kasancewa ta farko a rukuninta, da ba ta damar shiga zagaye na biyu.

Bisa jadawalin gasar, kungiyoyi 10 da suka zama matsayin farko a rukuninsu za su shiga gasar zagayen biyu a watan Nuwanba na bana domin fitar da kungiyoyi 5 da shiga gasar cin kofin duniya ta kasar Brazil a shekarar 2014. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China