in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Tanzania za ta karbi bakuncin wasan cin kofin kalubale na yankunan gabashin da tsakiyar Afrika
2011-09-29 15:07:36 cri
A ranar Larabar da ta gabata, wani babban jami'i mai kula da harkar wasan kwallon kafa na yankunan Afrika ya ce, kasar Tanzania za ta karbi bakuncin gasar wasan kwallon kafa na cin kofin kalubale na wannan shekara na yankunan gabashi da tsakiyar Afrika wanda za a fara daga ranar 24 ga watan Nuwamba zuwa 9 ga watan Disamba.

Da yake shaidawa kamfanin dillacin labarai na Xinhua ta wayar tarho daga sakatariyar kungiyar kwallon kafa ta yankunan gabashi da tsakiyar Afrika (CECAFA) a Nairobi, Nicholas Musonye wanda shi ne sakataren kungiyar ya ce, an riga an tsara komai na gasar wanda ya hadar da hada kan dukkan mambobin kungiyoyi wajen neman samun babban kofi da kuma kyautar kudade a lokacin ..

Sakataren ya ce, mambobi kasashen da za su shiga gasar sun hada Kenya, Uganda, Rwanda, Eriteria, Habasha, Burundi, Somaliya, Sudan, tsibirin Zanzibar na kasar Tanzania, sai da wasu bakin kasashe biyu wanda za su yanke shawarar shigarsu a sati mai zuwa.

A shekarar bara, kungiyar CECAFA ta gayyaci kasar Kamaru da Cote d'Ivoire a matsayin masu baki, sannan daga bisani ita ma kasar Zambia ta shiga gasar bisa gayyata.(Salamatu).

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China