in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ba a samu ci gaba a shawarwari tsakanin Palasdinu da Isara'ila ba, in ji firaminisatan Palasdinu
2013-11-29 11:06:31 cri

Firaministan Palasdinu Rami Hamdallah wanda ke ziyara a kasar Lebanon, ya bayyana a ran 28 ga wata a birnin Beirut cewa, shawarari tsakanin Palasdinu da Isra'ila da aka farfado da su a watan Yulin da ya gabata, ko alama ba su haifar da wani ci gaba ba. Ya ce bangarorin biyu ba su kai ga cimma matsaya daya ba, kan wasu manyan batutuwa ciki hadda batun 'yan gudun hijira, da na shata kan iyakar kasa, da batun masu aikata laifufuka da aka tsarewa a kurkuku, da batun albarkatun ruwa da kuma matsayin birnin Kudus.

Bisa labarin da kafar yada labaru ta kasar Lebanon ta bayar an ce, Rami Hamdallah ya gana da firaministan gwamnatin wucin gadin kasar ta Lebanon, inda suka tattauna kan halin da ake ciki a yankin gabas ta tsakiya, da dangantakar dake tsakanin Palasdinu da Isra'ila da dai sauran batutuwa.

Yayin taron manema labaru da aka yi bayan ganawar, Hamdallah ya bayyana cewa, Palasdinu za ta ci gaba da nacewa matsayin warware rikicin dake tsakanin bangarorin biyu, ta hanyar tabbatar da kafuwar kasashen Palasdinu da Isra'ila, yana mai fatan za a samu daidaito bayan shawarwarin.

Haka zalika Hamdallah ya yi kira ga wasu kasashe dake goyon bayan shawarwarin da ake yi ciki hadda Amurka, da su yi iyakacin kokarin taimakawa Palasdinawa ta fuskar kare hakkinta, ta hanyar kafa kasar Palasdinawa mai hedkwata a birnin Kudus, bisa shatin iyakar kasar ta shekarar 1967.

Game da matsugunan Yahudawa da Isra'ila ke ginawa a fiyalen Palasdinu kuwa, Hamdallah ya bayyana cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiwatar da manufofin kiyaye hakkin Palasdinawa, tare da kare zamantakewarsu, da ikon mallakar filayensu yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Kasar Isra'ila za ta saki kashi na biyu na Palasdinawa da take tsare da su 2013-10-29 10:18:29
v Mahmoud Abbas ya bayyana manyan batutuwa da za a tattauna kansu a zagaye na biyu na shawarwari tsakanin Palasdinu da Isra'ila 2013-08-16 15:54:55
v Amurka na kokarin maido da tattaunawa tsakanin Israila da Falasdinu 2013-07-23 15:46:08
v Sakataren harkokin waje ta kasar Amurka ya yi kira da a farfado da shawarwarin shimfida zaman lafiya tsakanin Palasdinu da Isra'ila 2013-07-18 17:19:47
v Ban Ki-Moon ya yi kira ga Palasdinu da Isra'ila da su daidaita matsala dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari 2013-02-06 14:33:43
v MDD ta bukaci Isra'ila da ta janye mazaunanta daga yankin da ta kwace daga hannun Palestinu 2013-02-01 11:01:39
v Jordan da Rasha sun jaddada cewa, kamata ya yi a sake yin shawarwari kai tsaye a tsakanin Palesdinu da Isra'ila 2013-01-13 16:38:13
v Wakilin Sin ya yi kira ga Isra'ila da ta bunkasa shawarwari da Falesdinu 2012-12-20 14:17:02
v Palasdinu ta tabbatar da mika bukatar ta na neman zama kasa 'yar kallo ta MDD 2012-11-28 10:15:54
v Isra'ila da Palasdinu sun tsagaita bude wuta daga daren 21 ga wata, in ji ministan harkokin wajen Masar 2012-11-22 15:17:28
v Rikicin da ya barke tsakanin Palasdinu da Isra'ila ya kara tsananta 2012-11-21 11:01:37
v Mataimakin shugaban Masar ya ce, kila ne Falesdinu da Isra'ila za su cimma matsayar tsagaita bude wuta 2012-11-20 14:56:31
v Mutane 69 sun rasu a sanadiyyar hare-haren da Isra'ila ta kai wa zirin Gaza da jiragen sama 2012-11-19 14:11:24
v AL ta kira taron musamman dangane da batun Palesdinu da Isra'ila 2012-11-18 17:11:52
v Palasdinu za ta ci gaba da neman samun amincewa daga MDD 2011-07-28 10:35:51
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China