in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban Masar ya ce, kila ne Falesdinu da Isra'ila za su cimma matsayar tsagaita bude wuta
2012-11-20 14:56:31 cri
A ran 19 ga wata, a yayin wani taron manena labaran da aka kira a fadar shugaban kasar Masar, mataimakin shugaban kasar da ke lura da harkokin waje da harkokin hadin gwiwar kasa da kasa, Essam Haddad ya bayyana cewa, kasar za ta dukufa matuka wajen dakatar da hargitsin da ke aukuwa tsakanin Falesdinu da Isra'ila, kuma ya nuna cewa, a daren ran 19 ga wata, kila ne za a tsagaita bude wuta tsakanin 'yan kungiyar Hamas ta Palestinu da dakarun Isra'ila.

Essam Haddad ya ce, Masar za ta yi iyakacin kokari wajen ciyar da ayyukan cimma burin tsagaita bude wuta tsakanin bangarorin biyu gaba, ta yadda za a iya samun zaman lafiya da kyakkyawan yanayi a yankin. Ya kara da cewa, a halin yanzu, Masar tana tattaunawa tare da Isra'ila da 'yan kungiyar Hamas, domin cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta, kuma bangarorin biyu suka fidda bukatunsu kan tsayar da musayar wuta, kuma sun gane muhimmancin tsayar da musayar wuta sosai. Essam Haddad ya kara da cewa, shugaban kasar Masar Morsi ya riga ya tattauna da shugaban kasar Amurka Obama kan rikici tsakanin Falesdinu da Isra'ila ta wayar tarho, inda ya bayyana cewa, kasar Amurka ta kasance kasar da ta fi kawo tasiri ga Isra'ila.(Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China