in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Isra'ila za ta saki kashi na biyu na Palasdinawa da take tsare da su
2013-10-29 10:18:29 cri

Kasar Isra'ila za ta saki kashi na biyu na Palasdinawa da take tsare daga ranar 29 ga wata a daf da wayewar garin ranar Laraba ranar 30 ga wata, gwamnatin Palasdinu za ta shirya shagulgula, amma shawarar da aka yanke ta sakin Palasdinawan ta haddasa bambancin ra'ayoyi a bangaren Isra'ila.

A wannan karo, za a saki Palasdinawa da yawansu zai kai 26, inda 21 daga cikinsu za su koma gidajensu da ke yammacin gabar kogin Jordan, a yayin da sauran palasdinawa 5 za su koma yankin Gaza. Bisa labarin da muka samu, an ce, yawancin Palasdinawan da za a sako a rukuni na biyu an fara tsare su ne kafin a daddale yarjejeniyar Oslo a shekarar 1994.

Shugaban Palesdinu Mahmoud Abbas ya bayyana cewa, za a kara sa kaimi ga Isra'ila da ta saki dukkan Palasdinawa da take tsare da su.(Danladi)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China