in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jordan da Rasha sun jaddada cewa, kamata ya yi a sake yin shawarwari kai tsaye a tsakanin Palesdinu da Isra'ila
2013-01-13 16:38:13 cri
A ranar 12 ga wata a Amman, babban birnin kasar Jordan, ministan harkokin wajen kasar Nasser Judeh ya gana da manzon musamman na ministan harkokin waje na kasar Rasha kuma shugaban sashen kula da harkokin yankin gabas ta tsakiya da arewacin nahiyar Afirka na ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sergei Vershinin, inda suka jaddada cewa, kamata ya yi a sake yin shawarwari kai tsaye a tsakanin Palesdinu da Isra'illa.

A cikin wata sanarwar da ma'aikatar harkokin waje ta kasar Jordan ta bayar a wannan rana, an ce, a yayin ganawar Judeh da Vershinin, sun yi musayar ra'ayoyi kan yadda za a sa kaimi ga samun zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya da kuma bunkasuwar yanayin da ake ciki a yankin, kuma sun jaddada cewa, za su yi kokari wajen tabbatar da ganin an kafa kasar Palesdinu mai cin gashin kanta a karkashin tsarin shirin warware rikicin a tsakanin bangarorin biyu, kuma ya kamata a sake yin shawarwari kai tsaye a tsakaninsu don cimma burin samun zaman lafiya a tsakanin bangarorin biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China