in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin ma'aikatan ceto na farko na kasar Sin ya isa kasar Philipines
2013-11-21 16:14:10 cri

Rukunin ma'aikatan ceto na farko da gwamnatin kasar Sin ta tura ya isa filin saukar jiragen sama na Ninoy Aquino dake birnin Manila hedkwatar kasar Philipines a daren jiya Laraba 20 ga wata, ban da haka, jirgin ruwa mai aikin jiyya da ake kira "ARK PEACE OF PLA" na kasar Sin shi ma ya tashi zuwa kasar Philipines a ran 21 ga wata da tsakar rana.

Rukunin ma'aikatan ceto da Sin ta tura a wannan karo yana kunshe da mutane 18, ciki hadda masu aikin ceto, masu aikin jiyya, masu ba da hidima. Shugaban rukunin Sun Shuopeng ya bayyana cewa, za su isa birnin Tacloban inda ya fi fama da hadarin cikin sauri, domin gudanar da aikin ceto a wuri na tsawon kwanaki 15. Idan kasar Philipines ta bukaci hakan, Sin za ta ci gaba da tura masu aikin ceto da masu aikin jiyya.

A sa'i daya kuma, rukunin ma'aikatan ceto na daban karkashen jagorancin Zhao Baige, mataimakin shugaba na farko na kungiyar Red Cross ta kasar Sin ya isa kasar a yammacin yau 21 ga wata. Ban da haka, kashi na 2 na rukunin ma'aikatan ceto dake kunshe da mutane 10 da kungiyar Red Cross ta kasar Sin ta shirya zai isa kasar a ran 23 ga wata domin ba da taimakon jiyya yadda ya kamata. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v Kenyatta ya lashi takobin daukar kwararan matakan kare hadurran mota a Kenya 2013-08-30 10:54:07
v Mutane 37 ne suka mutu a gabashin kasar Indiya sakamakon hadarin jirgin kasa 2013-08-19 20:48:25
v Ofishin jakadancin kasar Sin dake Amurka ya dufuka kan aikin daidaita hadarin jirgen saman da ya faru a birnin San Francisco 2013-07-08 16:36:05
v Ofishin jakadancin Sin a San Francisco ya tabbatar da mutuwar Sinawa biyu sakamakon wani hadarin jirgin sama 2013-07-07 16:35:04
v Mutane 15 suka hallaka a wani hadarin mota a kan iyakar kasar Sudan da Libya 2013-06-03 10:38:31
v Rundunar sojin sama ta Najeriya ta gano matuka jirgin sama da ya fado 2013-05-08 09:40:35
v Jirgin saman Najeriya ya fadi a Niamey, mutum biyu sun mutu 2013-05-07 09:46:22
v Mutane kimanin 50 sun mutu sakamakon wani rikici da ya barke a arewacin kasar Iraq 2013-04-24 15:15:46
v Mutane fiye da 60 sun mutu sakamakon fashewar da aka yi a wata ma'aikatar yin takin zamani ta Amurka 2013-04-18 16:43:47
v Mutane 43 sun rasu a sanadiyyar hadarin jirgin ruwa a Gabon 2013-03-22 15:01:45
v Hadarin jirgin ruwa ya hallaka sama da mutane 50 a Nigeria 2013-03-21 10:01:39
v Mutanen Sin sama da miliyan 6 suna fuskantar mahaukaciyar guguwa ta Haikui 2012-08-09 20:44:36
v Guguwa masu karfi sun sa an kawad da mutane dubu 549 a kasar Sin 2012-08-03 16:25:10
v Firaministan kasar Sin Wen Jiabao ya bukaci a mai da hankali sosai wajen magance mahaukaciyar guguwar iskar Saola da Damrey 2012-08-01 16:28:45
v Mahaukaciyar guguwa mai suna Nock-Ten ta yiwa mutane dubu 760 lardin Hainan da ke kudancin kasar Sin barna 2011-07-31 17:07:25
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China